Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Labarai

Yanzu-Yanzu: Gwamnonin Arewa da Sarakunan Gargajiya Sun Fara Taro a Kaduna

Published

on

Gwamna Uba Sani Na Karbar Taron Gwamnonin Arewa da Sarakunan Gargajiya a Kaduna

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna yana karbar taron Gwamnonin Jihohin Arewa da Sarakunan Gargajiya na yankin, wanda ke gudana a fadar gwamnatin jihar, Sir Kashim Ibrahim House, Kaduna.

Taron yana karkashin jagorancin Gwamnan Jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, wanda shi ne shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, shi ne ke jagorantar tawagar Sarakunan Gargajiya daga jihohin Arewa.

Manufar taron ita ce tattauna matsalolin tsaro, tattalin arziki da hadin gwiwar Arewa wajen ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Za mu ci gaba da kawo muku karin bayani yayin da taron ke gudana.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.