Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Dr. Saviour Enyiekere a matsayin Shugaban Hukumar Kula da Ayyukan Majalisar Ƙasa (NASC), tare da wasu kwamishinoni 12 da ke wakiltar yankunan siyasa shida na Najeriya.
Taron rantsarwar ya gudana a zauren majalisar, Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, kafin fara taron Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC).
Daga cikin waɗanda aka rantsar akwai tsohon Sanatan Kaduna ta Arewa, Sanata Suleiman Othman Hunkuyi, wanda ya wakilci yankin a Majalisar Dattawa daga 2015 zuwa 2019.
Hunkuyi wanda ya sauya sheka daga jam’iyyar NNPP zuwa APC kwanan nan, ya samu wannan mukami ne a matsayin wakilin yankin Arewa maso Yamma.
Shugaba Tinubu ya ja kunnen sabbin kwamishinonin NASC da su kasance masu gaskiya, ƙwarewa, da kishin ƙasa a yayin aiwatar da ayyukansu.
Ya ce hukumar na da muhimmiyar rawa wajen inganta ayyukan majalisa da samar da goyon baya ga ‘yan majalisa domin ingantaccen mulki.
A taron, an samu halartar Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, Sakataren Gwamnatin Tarayya George Akume, da wasu manyan jami’an gwamnati.