Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Labarai

Matsalar Ruwa Ta Kare a Maskawa: Hon. Munira Ta Kaddamar da Rijiyar Burtsatse Mai Hasken Rana

Published

on

Jama’ar garin Maskawa da ke cikin yankin Dan-Alhaji sun shiga cikin farin ciki da godiya bayan kammala aikin rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana (solar), wanda Hon. Munira Suleiman Tanimu ta kaddamar domin magance matsalar ruwa a yankin.

Hon. Munira, wacce ke wakiltar mazabar Lere East a Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, kuma ita ce Shugabar Masu Rinjaye, ta kaddamar da wannan aiki mai muhimmanci wanda ke samar da tsaftataccen ruwan sha ga daukacin al’umma – yara, manya da tsofaffi.

Rijiyar burtsatse ta dauke nauyin matsalar da ta dade tana addabar al’ummar Maskawa. Mutane sun fito kwansu da kwarkwatarsu suna murna da godiya, suna addu’ar Allah ya saka wa Hon. Munira, bisa wannan aiki na alheri da ta kawo.

Mai magana da yawun Hon. Munira, Ibrahim Munir, wanda shi ne S.A Media and Publicity ga Shugabar Marasa Rinji, ya bayyana cewa wannan aikin wani bangare ne na jajircewar Zinariyar Saminaka wajen ciyar da jama’a gaba.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.