Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Labarai

Mataimakiyar Gwamna Ta Jagoranci Taron Duba Ci gaban Jarin Dan Adam a Jihar Kaduna Karo Na Uku

Published

on

A yau ne aka gudanar da taron karo na uku na kwamitin dabarun bunkasa jarin dan adam da zuba jari na zamantakewa a jihar Kaduna, karkashin jagorancin Mataimakiyar Gwamnan jihar, Dr. Hadiza Sabuwa Balarabe.

Taron ya gudana a zauren taro na Mataimakiyar Gwamna da ke fadar gwamnati, Sir Kashim Ibrahim House.

An tattauna dabarun fadada shirye-shiryen tallafin gwamnati da nufin kai su ga al’umma da ba su da saukin samu, musamman a karkara da yankunan da ke bukatar kulawa ta musamman.

Mataimakiyar Gwamna Dr. Hadiza Balarabe ta jaddada kudirin gwamnatin jihar na ci gaba da inganta rayuwar al’umma ta hanyar zuba jari a bangaren lafiya, ilimi, abinci, da walwala.

Taron ya nuna yadda gwamnatin Uba Sani ke daukar cigaban jarin dan adam da matakin farko wajen gina jihar da kuma tabbatar da ci gaban da zai dore har abada.

Wannan taro na uku na daga cikin jerin kokarin da gwamnatin jihar Kaduna ke yi domin tabbatar da adalci da daidaito wajen raba albarkatu da inganta rayuwar al’umma, musamman matasa, mata da marasa galihu.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.