Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Lafiya

Kaduna Ta Kaddamar da Sabon Kwamitin BHCPF Don Inganta Kiwon Lafiya

Published

on

Gwamnatin Jihar Kaduna ta ƙaddamar da sabon kwamitin sanya ido da aka faɗaɗa kan Basic Health Care Provision Fund (BHCPF) domin inganta amfani da tallafin lafiyar jama’a.

An kaddamar da kwamitin ne a dakin taron Ma’aikatar Lafiya karkashin jagorancin Kwamishinar Lafiya, Hajiya Umma K. Ahmed. Ta bayyana cewa shirin BHCPF na da matuƙar muhimmanci wajen kula da lafiyar alumma, musamman mata da yara.

Hajiya Umma ta jaddada cewa faɗaɗa kwamitin na nuna irin ƙudurinsa Gwamna Uba Sani na tabbatar da gaskiya, adalci da haɗin kai a harkar lafiya. Ta bukaci mambobin kwamitin da su haɗa kai, su tabbatar da ingantaccen aiki da tsabtace tsarin kashe kudaden lafiya.

Kwamitin ya haɗa wakilai daga gwamnati, ƙungiyoyin raya al’umma, na addini, da kuma sarakunan gargajiya. Za su duba ayyukan cibiyoyin lafiya, su tabbatar da komai yana tafiya daidai.

Wannan mataki ya ƙara tabbatar da burin gwamnatin Kaduna na samar da ingantacciyar kulawa ta lafiya ga kowane ɗan jiha, ba tare da wariya ba.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.