Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Labarai

Kaduna na shirin karɓar zuba hanun jari na dala miliyan 300 a ma’adinai

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce tana shirye-shiryen karɓar zuba jari na dala miliyan 300 a fannin ma’adinai a jihar.

Gwamna Uba Sani ne ya bayyana haka bayan wata ganawa da ya yi da Colin Ikin, Manajan Darakta na kamfanin Atlantic Mining Techniques Ltd.

Gwamnan ya ce tattaunawar ta mayar da hankali kan haɓaka sashen ma’adinai na jihar, da kuma kafa katafaren kamfani da zai sarrafa ma’adinai a Kaduna.

Ya ce wannan wani bangare ne na ci gaba da aka samu bayan kafa masana’antar sarrafa Lithium a jihar – daya daga cikin na farko a Najeriya.

Gwamna Uba Sani ya ce Kaduna na da manyan albarkatu na ma’adinai, kuma tana da ƙa’idodi da rangwame da suka dace don jawo masu saka jari daga ciki da wajen Najeriya.

Ya ce gwamnati za ta ci gaba da kare duk wani jari da ke shigowa jihar, tare da tabbatar da zaman lafiya da sauƙin gudanar da kasuwanci.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.