Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Yajin Aikin ASUU-KASU 2025 Karo Na Biyu

Labarai

JAAC: Kaduna Ta Raba Naira Biliyan 11.67 Ga Kananan Hukumomi 23 na Watan Afirulu

Published

on

Gwamnatin Jihar Kaduna ta raba jimillar Naira biliyan 11.67 daga Asusun Tarayya ga kananan hukumomi 23 domin watan Afrilu, kamar yadda aka bayyana a taron Kwamitin Raba Kudaden Shiga (JAAC) karo na hudu.

Mataimakiyar Gwamna, Dr. Hadiza Sabuwa Balarabe, ce ta jagoranci taron wanda aka gudanar a Ma’aikatar Harkokin Kananan Hukumomi ranar Alhamis.

Kwamishinan Harkokin Kananan Hukumomi, Hon. Sadiq Maman Lagos, ya gabatar da rahoton jimilar kididigan kudin a gun taron.

Ya bayyana yadda aka raba kudaden kamar haka:

  1. Naira biliyan 5.31 – Rabon Doka (Statutory Allocation).
  2. Naira biliyan 5.92 – Rabon Harajin VAT.
  3. Naira miliyan 270.82 – Daga Harajin Canjin Kuɗi ta Intanet (Electronic Transfer Levy).
  4. Naira miliyan 182.65 – Karin Kudi (Augmentation).

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, cikin watan idan aka duba, kananan hukumomin jihar sun samar da Naira miliyan 18.83 a matsayin kudin shiga na cikin gida (IGR).

Taron ya samu halartar shugabannin kananan hukumomi 23, da kuma shuwagabannin hukumomi da sassan gwamnati da ke da ruwa da tsaki a JAAC.

Copyright © 2024 kaduna Reports.