Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Labarai

Hajjin 2025: Gwamna Uba Sani Ya Bukaci Alhazai Jihar Su Zama Jakadu Nagari

Published

on

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bukaci Alhazai 4,062 da ke shirin tafiya Hajji daga jihar da su zama wakilai Kaduna da Najeriya na gari a Saudiyya.

An bayyana hakan ne ta bakin mataimakiyar gwamna, Dakta Hadiza Balarabe, yayin kaddamar da jigilar farko na alhazan daga filin jirgin sama na Kaduna.

An nada Sarkin Kauru, Alhaji Ya’u Shehu Usman, ne Amirul Hajj na bana, domin kula da sauran jami’an aikin hajjin don samar da kula, jindadi da walwalar Alhazai jihar a kasa me tsarki.

Uwargidan gwamna, Hajiya Hafsat Uba Sani, ta shawarci Alhazai su bi umarnin malamai domin samun hajji mai karbuwa.

Jigilar farko da suka tashi sun hada da maniyata daga karamar hukumar Giwa da kuma yan hedikwatar hukumar hajji.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.