Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Yajin Aikin ASUU-KASU 2025 Karo Na Biyu

Labarai

Gwamnan Kaduna, Sanata Uba Sani, Ya Wakilci Shugaban Kasa a Jere don Fara Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano

Published

on

Gwamnan Jihar Kaduna, Mai Girma Sanata Dakta Uba Sani, ya isa garin Jere da ke karamar hukumar Kagarko domin wakiltar Shugaban Ƙasa, Mai Girma Bola Ahmed Tinubu, a wajen bikin kaddamar da aikin sake gina babban titin Abuja-Kaduna-Kano.

Titin da ake magana akai na daga cikin manyan hanyoyin da ke da matuƙar muhimmanci ga harkokin sufuri da kasuwanci a arewacin Najeriya, kuma aikin sake gina shi zai kawo sauƙi ga miliyoyin ‘yan ƙasa da ke amfani da hanyar kowace rana.

A wajen taron, an samu halartar manyan jami’an gwamnati da ‘yan siyasa masu tasiri a ƙasa, ciki har da Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi; Ministan Jiha na Ayyuka, Alhaji Bello Muhammed Goronyo; tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Alhaji Mukhtar Ramalan Yero; Sanata Danjuma Laah; da Sanata Suleiman Usman Hunkuyi.

Copyright © 2024 kaduna Reports.