Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Umarci Fitar Da Naira Biliyan 3.8 Don Biyan Hakokin ‘Yan Fansho

Published

on

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bayar da umarnin sakin Naira biliyan 3.8 domin biyan kudaden fansho, hakkokin ma’aikatan da suka mutu.

Gwamnan ya yanke wannan hukunci ne bisa tausayi da jin ƙai, bayan korafe-korafen da tsoffin ma’aikata da iyalan wanda suka mutu su ka yi dangane da yadda aikin tantance bayanan fansho ke shafar rayuwarsu.

Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa, duk da cewa aikin tantance bayanan fansho yana da matuƙar muhimmanci wajen kawar da masu karɓar fansho na bogi da kuma kare dukiyar jihar, yana da muhimmanci a saukaka wa waɗanda abin ya shafa.

“Wannan gwamnatin na da cikakken himma wajen kula da walwalar tsoffin ma’aikata. Sun sadaukar da rayuwarsu wajen gina jihar Kaduna, don haka wajibi ne a tallafa musu cikin lokacin ritaya,” in ji Gwamna Uba Sani.

Gwamna yana mai tabbatar da cewa gwamnatin sa za ta hanzarta kammala tantancewar domin tabbatar da biyan kudade ba tare da tangarda ba.

Tun bayan hawar Gwamna Uba Sani a watan Mayun 2023, gwamnati sa ta biya Naira biliyan 6.6 a matsayin fansho da sauran hakkokin ma’aikata da suka ritaya da kuma wanda suka rasu.

Ya yabawa tsoffin ma’aikatan bisa haƙuri, fahimta da goyon bayan da suke ba gwamnati, yana mai jaddada cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da sauke nauyin da ke wuyanta cikin gaskiya da adalci.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.