Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya nada sabbin kwamishinoni guda biyu tare da canja wurin aiki ga wani tsohon kwamishina, a wani mataki da gwamnatin ke cewa zai taimaka wajen inganta shugabanci da gudanarwa a fadin jihar.
A cikin sabbin nadin, Farfesa Abubakar Sani Sambo ya zama sabon kwamishinan Ilimi na jihar. Haka zalika, Gwamna Uba Sani ya kirkiri sabuwar Ma’aikatar Yada Labarai tare da tura tsohon kwamishinan ilimi, Farfesa Sani Bello (Mainan Zazzau), ya jagoranci ta.
Kazalika, Barrister Gloria Ibrahim ta samu mukamin kwamishinar harkokin matasa.
Farfesa Sambo, wanda ya shahara a fannin makamashi, ya rike mukaman mataimakin shugaban jami’a da shugaban jami’a a wasu manyan cibiyoyin karatu a Najeriya, ciki har da ATBU Bauchi da KASU. Ya kuma jagoranci Hukumar Makamashi ta Kasa daga 2005 zuwa 2012, sannan ya zama mai ba shugaban kasa shawara kan makamashi a 2011.
Barrister Gloria kuwa kwararriya ce a fannin lauya da sasanci. Ta shugabanci kamfanin Glownom Legal Consult a Kaduna, kuma memba ce a kungiyoyin NBA da FIDA da sauran ƙungiyoyin masu kare hakkin yara da matasa.
Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa yana sa ran sabbin kwamishinonin za su kawo sabbin dabaru wajen aiwatar da manufofin gwamnati, musamman a fannin ilimi da ci gaban matasa.