Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Tsaro

Gwamna Uba Sani Ya Jinjina wa Hukumar DSS Kan Kama ‘Yan Bindiga a Kaduna

Published

on

Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani, ta bakin Kwamishinan Shari’a na jihar, Sule Shuaibu (SAN), ya jinjinawa Hukumar DSS bisa cafke ‘yan bindiga da masu safarar makamai guda 54 a jihar.

Hukumar ta gudanar da ayyuka 34 da suka kai ga kama bata-gari daban-daban, ciki har da masu ba da bayanan sirri, masu safarar makamai, da masu satar mutane.

An kwato bindigogi da dama, ciki har da AK-47 guda biyar, GPMG guda daya, RPG guda uku, da harsasai sama da 5,000. Haka kuma, an ceto mutane 79 da aka sace.

Daga cikin wadanda aka kama akwai jami’in tsaro da aka samu da laifin satar harsasai 217 domin sayarwa ‘yan bindiga, da wani mai safarar harsasai 500 zuwa Birnin Gwari.

Gwamna Sani ya gode wa DSS karkashin jagorancin Mr. Oluwatosin Ajayi, tare da bukatar hadin kan al’umma domin dorewar zaman lafiya.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.