Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Jinjina wa Dangote Kan Bada Talafin Buhunan Shinkafa 35,000 a Kaduna

Published

on

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya nuna godiya ga Alhaji Aliko Dangote bisa agajin buhunan shinkafa 35,000 domin rabawa a dukan kananan hukumomi 23 na jihar.

Shirin, wanda Gidauniyar Dangote ta dauki nauyi, na daga cikin kokarin yaki da yunwa da talauci a Najeriya, karkashin Dangote National Food Intervention Project.

A jawabinsa da Shugaban Ma’aikatansa, Alhaji Sani Liman Kila, ya karanta, Gwamna Uba ya ce, “Wannan tallafi na nuna kulawa da tausayi, kuma yana goyon bayan manufofin gwamnatinmu na taimaka wa masu karamin karfi.”

Wakilin Gidauniyar Dangote, Alhaji Sadiq Ahmed, ya ce tallafin zai amfani fiye da mutane miliyan daya a Najeriya, kuma ya shafi dukkan kananan hukumomi 774.

“Tallafin yana nuni da yadda Gidauniyar ke daukar nauyin jin dadin al’umma a matsayin ginshikin ci gaba,” in ji shi.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.