Kungiyar malaman jami’a ta ASUU reshen Jami’ar Kaduna (KASU) ta dakatar da yajin aikin da ta fara tun ranar 24 ga Afrilu, 2025.
A wata takarda da ta aikewa shugaban jami’ar, kungiyar ta ce dakatarwar na nan take daga ranar Alhamis, 16 ga Mayu, 2025.
Takardar ta nuna cewa uwar kungiyar ASUU a matakin ƙasa ce ta amince da bukatar ASUU KASU na dakatar da yajin aikin domin ba gwamnati damar cika yarjejeniyar da suka cimma.
Kungiyar ta ce za su sake komawa taro ranar 30 ga Yuni, 2025 don duba matakin da gwamnati ta dauka kan aiwatar da yarjejeniyar.
ASUU KASU ta ce dakatar da yajin aikin ba yana nufin an magance matsalolin ba, sai dai suna ba gwamnati lokaci don ta gyara.
Rahoton ya kunshi sa hannun shugaban ASUU KASU na rikon kwarya, Dr. Abubakar Abdullahi da sakatare, Dr. Peter M. Waziri.