Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ta ce ta samu nasarar cafke mutane biyu da ake zargi da hannu cikin satar shanu a yankin kudancin jihar.
Mai magana da yawun bakin hukumar ’yan sanda reshen jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan ya tabatar da faruwar Lamarin, a rahoton da ya aika ma manema labarai a ranar laraba a Kaduna.
DSP Hassan, ya ce an samu nasarar kwato shanu 273 da ake zargin an sace su daga wasu guraren a Ishau dake karamar hukumar Piaikoro, border tsakanin jihar Kaduna da Niger.
Ya kara da cewa bincike ya nuna wasu daga cikin shanun sun fito ne daga Jihohin Katsina da Zamfara, inda aka dade ana fama da matsalar satar dabbobi.
ya bukaci jama’a da su ci gaba da ba da hadin kai domin ganin an shawo kan wannan matsala.