Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Siyasa

APC Sanga za ta marawa Tinubu da Uba Sani baya a 2027

Published

on

Jam’iyyar APC a karamar hukumar Sanga ta bayyana cikakken goyon bayanta ga Shugaba Bola Tinubu da Gwamna Uba Sani domin tsayawa takara a zaben 2027.

Wannan na zuwa ne bayan wani taron jam’iyyar da aka gudanar a Gwantu, inda manyan jiga-jigan gwamnati suka halarta, ciki har da mataimakiyar gwamna, Dr. Hadiza Balarabe; Hon. Ado Dogo; dan majalisa Hon. Gambo Dangana; da shugaban Sanga, Anto Usman.

Dr. Balarabe ta yaba da yadda gwamnatin Uba Sani ke sauya rayuwar jama’a, musamman da aikin titin Sanga-Jema’a da gwamnati ta fara. Ta bukaci mambobin jam’iyyar su hada kai domin cigaban APC.

Shugaban karamar hukumar, Anto Usman, ya ce mutanen Sanga za su mara wa gwamnan baya saboda irin ayyukan raya kasa da ya kawo musu.

Jam’iyyar ta ce hadin kai da cigaba na zamani ne ke jan ra’ayinsu wajen marawa shugabannin biyu baya.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.