Kungiyar malaman jami’oi ASUU reshen Jami’ar Jihar Kaduna (KASU) ta bayyana cewa sanarwar da shugaban jami’ar, Farfesa Abdullahi Musa, ya yi kan dakatar da yajin aikin kungiyar ba ta da tushe balle makama.
A wata takarda da shugabannin ASUU-KASU suka fitar ranar Alhamis, kungiyar ta ce ba shugabancin jami’ar ne suka kira yajin aikin ba, don haka ba ta da hurumin dakatar da shi.
Takardar, wadda shugaban rikon kwarya na ASUU-KASU, Comr. Abubakar Abdullahi da sakataren kungiyar, Comr. Peter Waziri, suka sanya wa hannu, ta bayyana cewa har yanzu kungiyar na jiran Bayanai daga (NEC) dangane da matakin da aka cimma a taron gaggawa da aka gudanar a ranar 15 ga Mayu, 2025.
ASUU-KASU ta shawarci jama’a da su yi watsi da sanarwar da aka ce jami’ar ta fitar, tana mai jaddada cewa dakatar da yajin aiki ba zai yiwu ba sai da umarnin uwar kungiyar ta kasa.