Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Labarai

Gwamna Uba Sani ya kaddamar da masana’antar lithium ta farko a Najeriya

Published

on

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya kaddamar da masana’antar sarrafa lithium ta farko a Najeriya.

Masana’antar, wadda ke Kangimi kan hanyar Kaduna-Jos, za ta rika sarrafa ma’adinan lithium fiye da ton 30,000 a rana.

Kwamishinan Muhalli da Albarkatun Kasa, Abubakar Buba, ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a gidan gwamnatin jihar.

Wannan mataki na daga cikin shirye-shiryen gwamnatin jihar na bunkasa tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da kuma dakile hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba.

Gwamnatin ta ce wannan masana’anta na daga cikin matakan da gwamnati ke dauka domin kara janyo masu zuba jari da kuma samar da ayyukan yi ga matasa a fadin jihar.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.