Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Labarai

Gwamnonin Arewa da Sarakuna Sun Cimma Sabbin Matakai Kan Tsaro a Kaduna

Published

on

A ranar Asabar, 10 ga Mayu, 2025, Gwamnonin Arewa da Sarakunan Gargajiya sun yi taro a Kaduna domin tattauna matsalolin tsaro da sauran kalubale da suka addabi yankin.

An gudanar da taron ne a fadar Sir Kashim Ibrahim House, Kaduna. Gwamnonin jihohi 19 na Arewa da shugabannin Majalisun Sarakunan jihohin suka halarta.

Bayan dogon shawarwari, sun cimma matsaya a kan wasu muhimman abubuwa:

Yabo ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa kokarinsa wajen magance matsalolin tsaro da gine-gine a Arewa.

Shawara ta hada kai da Gwamnonin Najeriya don tallafa wa jami’an tsaro.

Karfafa hanyoyin tsaro na cikin gida a jihohi.

Kafa sabbin tsarin sa ido tsakanin jihohi, musamman a kan iyakoki.

Goyon bayan kafa ‘yan sanda na jihohi da kira ga Majalisar Tarayya da ta hanzarta dokar da zata ba da dama.

An shirya cewa taron na gaba zai gudana ranar 30 ga Agusta, 2025.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.