Connect with us
Blinking Dot and Text
Ku Saurare Mu Kaitsaye
Kai Tsaye:
Babu sabbin labarai a yanzu.

Labarai

Hon. Munira Suleiman ta Gabatar da Kudirin Dokar Kafa Kwalejin Kimiyyar Noma da Muhalli a Saminaka

Published

on

Yar majalisar jihar dake wakiltar jama’ar Lere ta gabas, Hon. Munira Suleiman Tanimu shugaban masu rinjaye a majalisar jihar Kaduna, ta Gabatar da Kudirin Dokar Kafa Kwalejin Kimiyyar Noma da Muhalli ta Saminaka.

A zaman majalisar dokoki ta jihar Kaduna da aka gudanar a ranar litini, an gabatar da muhimman kudirin dokoki da dama wadanda suka samu karatu na farko da na biyu.

A cikin zaman, an gabatar da Kudirin Dokar Kafa Kwalejin Kimiyyar Noma da Muhalli a Saminaka. Kudirin, wanda Hon. Munira Suleiman Tanimu ta dauko, ya samu karatu na farko ba tare da tsaiko ba.

A yanzun haka majalisar ta dage zamanta sai ranar 13 ga watan mayun 2025.

KA/KI NA DA LABARI ?

Muna maraba da labarai daga gare ku. Idan ka/ki na da wani abu da ya dace da wallafa, a turo mana ta imel:

kadunareports@gmail.com

Copyright © 2024 kaduna Reports.